Wata Sabuwa! Kundin Tsarin Mulkin Najeriya Bai Ba wa Sarkin Musulmi Ikon Nada Hakimai Ba – In ji Gwamnatin Sokoto

FB IMG 1719098884596

Gwamnatin jihar Sokoto ta ce a kundin tsarin mulkin Najeriya, Mai Alfarma Sarkin Musulmai bashi da ikon nada kowa a kowanne irin mukami.

Alfijir labarai ta ruwaito da yake jawabi a yayin taron jin ra’ayin al’umma kan dokar masarautu ta 2008, kwamishinan shari’a na jihar Sokoto, Barrister Nasiru Binji ya ce dokar masarautu da ake da ita a jihar ta ci karo da kundin tsarin mulkin Najeriya.

Ya ce sashi na 76(2) na dokar ya ci karo da sashi na 5(2) na kundin tsarin mulkin Najeriya.

“Sashi na 5(2) na kundin tsarin mulki ya bayyana karara, ikon nadawa na hannun Gwamna kai tsaye ko ra hanyar mataimakinsa ko jami’in Gwamnati da aka dorawa alhakin hakan.

“Don haka babu wani iko da aka baiwa Sarkin Musulmai na tin nadi”, inji kwamishinan.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇

https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *