Gwamna Ahmed na Sokoto ya samu amincewar majalisar zartaswar jihar domin mika wani kudiri ga majalisar dokokin jihar da ke neman yin gyara ga dokar da ake da ita na nadi da tsige sarakunan gargajiya a jihar Sokoto.
Alfijir labarai ta ruwaito Za a gabatar da kudrin don yin tambari wato amincewa da shi a ranar Litinin
Mafi yawa, kudirin na neman a kwacewa sarkin musulmi gaba daya ikon nadawa, dakatarwa, hukuntashi, mika mulki da dai sauransu, duk wani basaraken gargajiya har zuwa mai unguwa.
Hakan na nufin iko zai kasance ga gwamna gaba daya ba tare da tuntubar kowa ba. In da Ranka ka sha Kallo.
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇
https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj