Anyi Jana’izar Mutum 4 Cikin Wanda Masu Garkuwa Suka Harba A Zariya

IMG 20231007 WA0146

Da misalin karfe 10 na safiyar Asabar 7/10/2023 , aka gabatar da sallar jana’izar mutum hudu wanda Mahara (kidnappers) suka kashe nan take a daren jiya juma’a, a Unguwan Dankali dake yankin Dan magaji a Zariya .

Alfijir Labarai ta rawaito yan ta’addan sun bayyana ne da misalin karfe 11 na dare , inda suka mamaye gidan Alh Musa ( Dan haki) basu sameshi shi ba, suka tafi da É—aya daga cikin matan shi , da sauran mata guda uku, sunyi ta barin wuta da bindigogi, sun harbi kusan mutum 9, inda mutum 4 suka rasu , mutum 5 kuma na Asibiti.

Dubban al umma ne suka halartarci jana’izar cikin alhini da da damuwa. limamin unguwar Malam Musa Tanko shine yajagoranci jana’izar.

Cikin taimakon Allah duka mata hudu da yan ta’adda suka dauka Allah ya kubutar dasu.

Muna rokon Allah ya jikan wanda suka rasu, ya baiwa masu rauni lafiya sannan yayi mana Maganin wannan musiba ameen

IMG 20231007 WA0144
IMG 20231007 WA0145

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai 👇

https://chat.whatsapp.com/K8z1chFesJeCf99QehWJPo

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *