Ɗan Adaidaita Sahu ya Mayar Da Kuɗin Da Ya Tsinta Har Miliyan 15 da Ya Tsunta ga Mai su

Na koma, da na isa wurin ban same shi ba, kuma na ci gaba da bincike amma ban iya ganinsa ba.

Alfijir Labarai ta rawaito wani matashi dan shekara 22 mai suna Auwalu Salisu ya mayar da kudi har Naira miliyan Sha biyar (15) ga wani fasinja da ya zo daga kasar Chadi sayan kaya a Kano ya manta a Adaidaita sahunsa.

Salisu ya mayar da kudin ne bayan an sanar da bacewarsu a wani gidan rediyo a Kano.

Matashin ya shaida wa gidan rediyon cewa bai lura fasinjan nasa ya manta da kudin ba har ya isa gida.

Isar sa gida ke da wuya, ya labartawa iyayensa abin da ya faru tare da gabatar da makudan kudaden gare su, nan take iyayen suka umarce shi da ya je ya nemo mai kudin domin a bashi kudin sa.

“Na dauki mutumin daga Badawa zuwa Bata.

Na koma da na isa wurin, ban same shi ba kuma na ci gaba da bincike amma ban iya ganinsa ba.

“Na koma gida na ba mahaifiyata kuɗin da ta ajiye a cikin tufafinta.

Na ji tsoro domin ina ɗokin mayar da kuɗin ga mai shi.

..Ba ni da niyyar taba ko da kwabo, domin ba nawa ba ne, kamar yadda aka haramta mani, ”in ji Auwalu.

Matashin, wanda ya samu rakiyar iyayensa ya ce ba shi da niyyar taba kudin duk da halin da suke ciki a gida na hannu baka hannu kwarya.

“Da kyar muke dora tukunya sau biyu a rana, ko jiya ma ba mu iya yin girki ba yayin da kudin ke tare da mu,” Kamar yadda mahaifinsa ya fada.

A nasa bangaren, mai kudin, Wanda yai magana ta bakin dan uwansa Musa Hassan, ya ce bai taba tunanin akwai mutanen kirki irin wannan yaron a duniya ba, ya godewa Allah sannan ya godewa mai Adaidaita sahun Auwalu da Kuma iyayensa bisa tarbiya da suka ba shi, nan take ya baiwa matashin tallafin kudi naira Dubu Dari Hudu (N400,000) domin nuna godiyarsa.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai  👇

https://chat.whatsapp.com/FNim39ly65N2CzcTt8FgWb

2 Replies to “Ɗan Adaidaita Sahu ya Mayar Da Kuɗin Da Ya Tsinta Har Miliyan 15 da Ya Tsunta ga Mai su

  1. AlhamduliLLAH
    Wannan yaro Allah Ya albarkaci rayuwar sa Allah ya kara dora shi akan tafarki madaidaici. Iyayen da suka yi tarbiyyar shi suma Allah Ya basu lada ya kuma rufa musu asiri.
    Kyautar da aka bashi kuma Allah Ya yalwanta mishi ita.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *