Alfijr ta rawaito Mutane 7 ne suka mutu, wasu 23 kuma suka jikkata bayan ruftawar wani filin wasanni na makaranta a arewacin kasar Thailand.
A cewar ma’aikatar rigakafin Ibtila’i (DDPM), hatsarin ya afku ne da misalin karfe 7:00 na dare, agogon kasar a ranar Litinin lokacin da rufin filin wasan motsa jiki na makarantar firamare a lardin Phichit ya ruguje sakamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya.

Firayim Minista Prayut Chan-o-cha ya jajantawa iyalan wadanda abin ya shafa tare da umurtar hukumomin da abin ya shafa da su ba da fifiko wajen neman wadanda suka bata.
Anucha Burapachaisri, mataimakin babban sakataren firaminista kuma mai magana da yawun gwamnati, ya ce ana kokarin tantance irin barnar da aka yi tare da bayar da agajin gaggawa ga wadanda abin ya shafa.
An kai mutanen da suka jikkata zuwa asibitoci biyu na yankin, in ji DDPM a shafinta na Facebook.

Rahotannin da kafafen yada labarai na cikin gida suka fitar na nuni da cewa wata guguwa ta afkawa rufin karfen ginin, lamarin da ya yi sanadiyar rugujewar ginin gaba daya.
Gwamnan jihar Phichit Payon Asavapichayon ya ziyarci wurin da lamarin ya shafa a ranar Talata, inda akalla gidaje 100 aka bayar da rahoton barnar ta illata, sakamakon guguwar.
Yayin da aka fara damina, ma’aikatar yanayi ta kasar Thailand ta yi hasashen samun ruwan sama mai karfi da ci gaba a galibin yankunan kasar.
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
Facebook. Alfijr Labarai
YouTube. Best Seller Channel
Twitter. @Musabestseller
Instagram. @musa_bestseller
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇
https://chat.whatsapp.com/GdLiqZyHuSz5NhjdGoGRGZ