Zamu yi wa Amurka lahanin da ba zai gyaru ba idan ta kai mana hari – In Ji Ayatollah

FB IMG 1750249234576

Jagoran Addinin Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya yi gargaɗi cewa Iran za ta mayar da mummunan martani idan Amurka ta ɗauki matakin soji kan ƙasar.

Cikin wata sanarwa da jagoran ya fitar, aka kuma karanta a gidan talbijin na ƙasar, Ayatolla ya ce Iran ba za ta lamunci hari daga Amurka ba.

“Idan Amurka ta yi amfani da karfin soja, za ta fuskanci lahani da ba za a iya gyarawa ba.”

“Mutane masu hikima waɗanda suka san Iran da mutanenta da tarihinta, (sun san cewa) ba a yi musu barazana, domin Iraniyawa ba mutane ne da ke miƙa wuya ba,” in ji Khamenei a cikin sanarwar.

BBC

Domin bada talla ko shawarwari a iya kiranmu a wannan lambar +2348032077835

For more information about Alfijir labarai/Alfijir news fallow here 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/KoLt2IMlnQfJPP6zNrcNKD

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *