Shugaba Tinubu Zai Naɗa Ganduje Jakadan Najeriya

FB IMG 1723726596754

Shugaba Bola Tinubu ya bayar da shawarar a nada Abdullahi Ganduje, shugaban jam’iyyar APC mai mulki na kasa a matsayin jakada a wata kasa ta Afrika da ba a bayyana ba,

Alfijir labarai ta ruwaito wasu majiyoyi da suka nemi a sakaya sunansu sun tabbatar da cewa tun farko dai shugaba Tinubu ya dorawa shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio aikin mika wa Ganduje tayin jakadan.

A cewar wadannan majiyoyin, Akpabio ya sanar da Ganduje cewa an nada shi ne domin a samar masa da mukamin diflomasiyya a matsayin hanyar dakile tasirin shari’ar cin hanci da rashawa da ake yi masa a Kano.

Ganduje wanda ke fuskantar tuhumar cin hanci da rashawa da suka hada da sama da Naira biliyan 50 tare da matarsa, dansa, da sauran mukarrabansa, jama’a sun fara bin diddigin badakalar cin hanci da rashawa a shekarar 2018. Duk da tuhumar da ake masa, Ganduje ya nuna rashin jin dadinsa tare da yin watsi da tayin a fakaice, inda ya ce tuhumar da ake yi masa na “kayan karya ne” kuma ya bayyana aniyarsa ta wanke sunansa a kotu.

“Shin haka ne shugaban kasa ke ba da amanata? Ban da haka, na tsufa da zama jakadanci. Duk tuhume-tuhume na karya ne, kuma zan ci nasara a shari’a a kotu,” inji Ganduje ya mayar da martani ga Akpabio.

Daga bisani, shugaba Tinubu da kan sa ya tattauna batun nadin jakadan da Ganduje, inda ya ba shi zabin ya zabi “kowace kasa a Afirka.” Sai dai wasu majiyoyi na nuni da cewa shugaban ya gabatar masa da zabin da za a yi a Afirka, Asiya da Turai.

Wata majiya da ke kusa da Shugaban APC ta bayyana cewa, zabin da Tinubu ya fi so shi ne kasar Chadi, ganin yadda Ganduje ya goge a matsayin babban sakataren Hukumar Tafkin Chadi daga 2009 zuwa 2011.

“Shugaban kasa na neman hanyar da zai gamsar da Ganduje, shi ya sa ya ba shi zabi a tsakanin kasashe uku. Duk da haka, abin da shugaban yake so na Chadi ne, “in ji majiyar.

KBC Hausa

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇

https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *