Da  Ɗuminsa: CBN Ya Buƙaci Bankunan Da Su Riƙa Fitarwa Da Karɓar Tsofaffin Takardun Kuɗin Naira

Alfijr ta rawaito Gwamnan babban bankin na CBN, Godwin Emefiele ya bayar da wannan umarni a taron kwamitin bankunan da aka gudanar a ranar Lahadi, 12 ga Maris, 2023.

A cewar umarnin, masu ba da lamuni a bankunan kasuwanci su samar da lambobin ajiyar kudi kuma babu iyaka ga adadin na lokuta mutum ko kamfani na iya yin ajiya.

Da yake tabbatar da ci gaban a safiyar Litinin, 13 ga Maris, 2023, gwamnan jihar Anambra, Charles Soludo ya ce; “Emefiele da kan sa ya tabbatar min da abin da ke sama a yayin tattaunawa ta wayar tarho a daren Lahadi”.

Gwamnan ya bukaci mazauna jihar Anambra da su karbe tare da yin mu’amala da tsofaffin takardun kudi (N200; N500; da N1,000) da kuma sabbin takardun kudi.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

Facebook.   Alfijr Labarai
YouTube.     Best Seller Channel
Twitter.        @Musabestseller
Instagram.  @musa_bestseller

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 

https://chat.whatsapp.com/G1wNveF9mGU7jec5mWhFvZ

One Reply to “Da  Ɗuminsa: CBN Ya Buƙaci Bankunan Da Su Riƙa Fitarwa Da Karɓar Tsofaffin Takardun Kuɗin Naira”

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *