Alfijr ta rawaito ɗan ƙasar China da ake zargi da kashe budurwarsa ‘Ummita’ a jihar Kano ya fara gabatar da shaida a shari’ar da ake yi masa.
Hakan ya zo ne bayan masu ƙara sun kammala gabatar da na su shaidun a gaban babbar kotun jihar.
Mai shari’a Sanusi Ado Ma’aji ya ci gaba da sauraren tuhumar da ake yi wa Mista Geng Quangrong da kashe tsohuwar budurwarsa Ummulkhuksum Sani Buhari wadda aka fi sani da ‘Ummita’ a yau Laraba.
Ɗan China da kansa ya tsaya a gaban kotun a matsayin shaida, ya zayyanawa kotu haɗuwarsa da sahibarsa Ummulkhuksum.
Ya ci gaba da cewa, wata ƙawarta ce ta ba ta lambarsa ta kira shi cewa tana ƙaunarsa kuma za ta aure shi, shi kuma ya amince da jin wannan batun.
Bayan ɗan wani lokaci suna soyayya tare ya dinga yi mata hidimar maƙudan Kuɗaɗe, bisa alkawarin za su yi aure! Amma sai ta ke ƙasa ƙasa taki auren nasa, inda ta auri wani amma duk da haka lokaci zuwa lokaci tana kiransa su gaisa ta nemi kuɗi ya ba ta. In Ji shi.
Hakazalika ‘ya bayyana cewar aƙalla ya kashe mata naira miliyan 60, wanda suka hada da siyen mota, fili, jarin kasuwancin da take yi.
Ya kuma tabbatar da akwai bayanan banki na kuɗin da ya kashe mata, wanda idan an karɓo su daga banki za su tabbatar da hakan, in ji lauyan mista Geng.
Mista Geng ya ci gaba da cewa ya taɓa ba ta naira miliyan 10 ta sayi mota, amma sai ta yi amfani da kuɗin ta sayi fili a Abuja ta fara gini a 2021.
Amma daga ƙarshe saboda ba ta son ta aure shi sai ta ce ba ta karɓi komai daga hannun sa ba.
Ya kuma shaidawa kotun cewa a ranar 13 Satumba 2022 ta buƙaci ya bata kuɗi ta kammala aikin ginin ta a Abuja.
Nan shi kuma ya faɗa mata cewa ba shi da kuɗi abin da ya fusatata ta daina ɗaukar wayarsa.
Ya kara da cewar duk maganar da suka yi tana cikin WhatsApp dinsa.
Mista Geng yace yana matuƙar ƙaunar Ummulkhuksum, ba ya son ɓacin ranta.
Sannan ya faɗa wa kotun cewa ta rika yin ƙorafin cewa ba ya kashe mata kuɗi kamar baya indan ta nema.
Daga bisani kuma ta faɗa masa cewa ta samu wani mutum da suke soyayya har ma ta aika masa da hotunan sabon saurayinta, al’amarin da ya ba shi haushi.
Hajiya Aisha Mahmud darakta ce a ma’aikatar shari’a ta jihar Kano ta yi ƙarin haske bayan fitowa daga kotun.
”Tun wancan zaman da muka ce mu mun rufe sai ya nemi kotu da ta ba shi damar ya sake kirowa shaidunsa, tare da neman kotu da ta sake kirawo shaidun da muka gabatar, inda ka kira mahaifiyar yarinyar ta zo ya yi mata tambayoyi, da ɗan sanda shi ma ya zo ya yi masa tambayoyi”
”Mu ba mu san yawan sahidun da zai kira ba, yau dai ya fara, to sai goben in ya gama kiran shaidun nasa, zai rufe gobe”, inji Hajiya Aisha
Alkalin babbar kotun mai shari’a Sanusi Ado Ma’aji ya ɗage zaman kotun zuwa gobe goma sha biyu ga wannan watan don ci gaba da sauraron Mista Geng kan abin da ya faru tsakaninsa da Ummita, wadda ake zargin ya kashe ta.
BBC
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
Facebook. Best seller Channel
YouTube. Best Seller Channel
Twitter. @Musabestseller
Instagram. @musa_bestseller
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇
Kowa yahau motar kwadayi zata saukeshi atashar wolaqanci to Amma shida akadaukoshi aiki nawani Atuhumeshi Aina yasami kudi har million 60 din dayakashe mata Allah de yasan shirinsu Amma kisan dayayimata yashafe million 60 dinsa in shariar gaskiya zaayi Toh Sharia sabanin hankali