Majalisar Wakilai Ta bukaci A dakatar da Sabon Harajin Internet

FB IMG 1715268720230

A Yau Alhamis, 9 ga watan Mayu, Majalisar Wakilai ta bayar da umarnin dakatar da Babban Bankin na CBN da gaggawar dakatar da aiwatar da harajin ta yanar gizo da babban bankin ya kaddamar, kamar yadda dokar ta tanada.

Alfijir labarai ta rawaito majalisar ta nuna damuwarta kan yadda ‘yan Najeriya zasu iya fahimtar harajin da babban bankin ya fitar, domin bai yi daidai da ka’idojin da ke kunshe a cikin sashe na 44 (2a) na dokar aikata laifuka ta yanar gizo ba dangane da masu karbar harajin.

A martanin da shugaban marasa rinjaye Kingsley Chinda (PDP, Rivers) ya gabatar a madadin daukacin mambobin majalisar, Majalisar ta bukaci babban bankin kasar da ya gaggauta janye takardar da ta bayar a baya dangane da aiwatar da harajin, maimakon haka ta fitar da wata sabuwar takardar da ta yi daidai da tanadin dokar.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇

https://chat.whatsapp.com/IUuk7jeH4yvAkwOmbOCSfl

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *