Da Dumi Duminsa! Kudin Aikin Hajji A Najeriya Ya Koma Miliyan 8.2

Screenshot 20240310 210256 com.facebook.katana edit 1808895184618

Daga Aminu Bala Madobi

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta kara kudin jigilar maniyyata aikin hajjin bana zuwa kasar Saudiyya da N1,918,032.91, inda ta sanya ranar 28 ga Maris, 2024.

Alfijir labarai ta rawaito hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar Fatima Sanda Usara ta sanya wa hannu a karshen mako.

Hukumar ta alakanta wannan ci gaban da matsalar tabarbarewar kudin waje da Najeriya ke fama da shi tsawon watanni.

Idan dai za a iya tunawa dai tun da farko NAHCON ta bayyana kudin aikin Hajjin bana a kan Naira miliyan 4.9, inda masu ruwa da tsaki da dama suka yi kira ga Gwamnatin Tarayya ta kawo dauki.

Sai dai a ranar Lahadin da ta gabata, hukumar ta bukaci wadanda suka biya kudin farko da su kara Naira Miliyan 1.9, akan adadin dasuka biya na Naira miliyan 6.8.

“Dangane da aikin Hajjin 2024 kuwa, jadawalin shirye-shiryen da ma’aikatar Hajji da Umrah ta Saudiyya ta fitar ta fara da wuri kamar yadda aka saba kuma ana sa ran kammala shi kafin lokacin da aka saba yi.

“Duk da haka, ba a jinkirta tura kudin aikin Hajji da wadanda abin ya shafa suka yi gyara ba, wanda ya haifar da sauyi sau biyu a ranar 12 ga watan Fabrairun 2024.

Idan zaku iya tunawa cewa a ranar 31 ga Disamba 2023, Dola 1 tana Naira N897:00 abin takaici, sun sa wa’adin tattara kuɗin Hajji ya ragu bayan daidaita farashin canji na ƙasashen waje, wanda ya gabatar da wani sabon ƙalubale.

“Maniyyatan aikin hajji a Najeriya a yanzu za su fuskanci karin tsadar kudin aikin Hajji, duk da cewa sun riga sun biya kayyadadden farashin kudin aikin Hajji. Naira miliyan 4.9.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai 👇

https://chat.whatsapp.com/CJ2q8cmhhOxFY6OEgwV5vk

One Reply to “Da Dumi Duminsa! Kudin Aikin Hajji A Najeriya Ya Koma Miliyan 8.2”

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *