Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta ce gobara ta kone shaguna 37 a unguwar Zawaciki da ke karamar hukumar Kumbotso a jihar .
Alfijir labarai ta rawaito kakakin hukumar, Saminu Abdullahi ne ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN cewa gobarar ta faru ne da misalin karfe 01:37 na safiyar Laraba.
A cewar Abdullahi, da misalin karfe 01:37 na safe ne wani Malam Baba yayi musu waya cewa gobara ta tashi a kasuwar dake Zuwaciki.
“Mun yi gaggawar tattara jami’an mu zuwa wurin da abin ya faru da misalin karfe 01:47 na safe, muka kashe gobarar domin kada ta bazu zuwa wasu shaguna,” inji shi.
Abdullahi ya ce shagunan 37 sun kasance a kasan bene na wani gini dake kasuwar.
Ya kara da cewa wasu shaguna uku ne gobarar ta dan yi barna.
A cewar sa, ba a samu asarar rai ba, kuma ana kan binciken musabbabin tashin gobarar.
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai 👇
https://chat.whatsapp.com/CJ2q8cmhhOxFY6OEgwV5vk