Muneer Ibn Ibrahim shi ne mai gidan hayar da suke, ya sheda cewa, wani firinji ne yai sanadin tashin gobarar bayan ya kama da wuta
Alfijir labarai ta rawaito wani magidanci mai suna Shu’aibu Ahmad mazaunin unguwar Tudun Wada Brigate a karamar hukumar Nassarawa a birnin Kano, ya rasa ransa tare da matar Binta da ‘yayansu guda 5.
Hakan ya faru ne sakamakon tashin wata mummunar gobara da ta afku sabadiyar kawo wutar lantarki mai karfin gaske da misalin karfe 12 na daren Lahadin da ta Gabata.
Muneer Ibn Ibrahim shi ne mai gidan hayar da suke, ya sheda cewa, wani firinji ne yai sanadin tashin gobarar bayan ya kama da wuta a lokacin da aka kawo wutar, shi kuma marigayin da iyalansa suna bacci ษakin nasu kuma a rufe.
Wannan dalilin ya jawo hayaki ya turnike su inda hakan yai sanadiyar mutuwarsu su bakwai lokaci daya.
An yi jana’izarsu Kamar ya ddaaddini ya tanadar.
Allah ya jikansu da rahama Allah ya kyautata makwancinsu.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai ๐๐
https://chat.whatsapp.com/IUuk7jeH4yvAkwOmbOCSfl