Mutane 2, Sun Mutu 56 Suka Jikkata A Wata Mummunar Fashewar Iskar Gas

Galibin wadanda suka jikkata ‘yan kwana-kwana ne da suka garzaya tashar domin kashe gobarar daga fashewar farko kafin ta biyun ta faru.

Alfijir Labarai ta rawaito Mutane 2 ne suka mutu yayin da wasu 56 suka jikkata bayan wasu bama-bamai biyu sun tashi a wata tashar sarrafa iskar gas mara lasisi da ke arewacin Bucharest babban birnin kasar Romania a yammacin jiya Asabar, in ji jami’ai.

Galibin wadanda suka jikkata jami’an kashe gobara ne da suka garzaya tashar domin kashe gobarar da fashewar ta farko ta tashi kafin ta biyun ta faru.

Mutanen biyu da suka mutu ma’aurata ne, kamar yadda shugaban sashen gaggawa Raed Arafat ya shaidawa manema labarai a ranar Lahadi.

Mutumin ya samu bugun zuciya, yayin da matar ta mutu bayan da ta samu munanan kuna, in ji shi.

Daga cikin wadanda suka jikkata – wasu da suka samu munanan konewa – sun hada da ‘yan kwana-kwana 39, da jami’an ‘yan sanda biyu da jami’an Jandarma guda biyu, a cewar Arafat.

“A cikin dare mun tura ma’aikatan kashe gobara biyu da farar hula biyu zuwa kasashen waje (don jinya) kuma wasu za su biyo baya,” in ji shi.

An kai mutanen hudu zuwa Italiya ko Belgium, a cewar ma’aikatar tsaro.

Romania ta nemi taimako ta hanyar Tsarin Kariyar Jama’a na EU don kula da marasa lafiya 18 da suka kone, in ji Kwamishinan Kula da Rikicin Turai Janez Lenarcic a kan X, wanda aka fi sani da Twitter.

Austria, Jamus da Norway sun ba da taimako, in ji Lenarcic.

Har yanzu dai ba a bayyana dalilin da ya haddasa tashin bama-baman a cikin garin Crevedia, kuma masu gabatar da kara sun bude wani bincike.

“Mun san cewa tashar ba ta aiki, don haka a fili ba ta da izinin yin aiki,” in ji Arafat.

Gobarar ta kuma tilastawa kwashe mutanen da ke cikin nisan mita 700 (yadi 770).

“Na yi matukar bakin ciki cewa fashewar a Crevedia ya haifar da wadanda abin ya shafa,”

Shugaba Klaus Iohannis ya rubuta a shafin Facebook, yana mai cewa “abin takaici ne”.

Haushi ya sha kara kamari a cikin Tarayyar Turai saboda rashin sa ido a hukumance don tabbatar da bin ka’idojin tsaro.

A shekara ta 2015, wata gobara ta tashi a wani gidan rawa na Bucharest, bayan da aka harba wasan wuta, inda mutane 64 suka mutu.

Channel

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

Facebook. Alfijir Labarai
YouTube. Best Seller Channel
Twitter. @Musabestseller
Instagram. @musa_bestseller

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai 👇

https://chat.whatsapp.com/Jmw5CBsPV6H3DbSgnlFUHM

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *